MEKE FARUWA Littafi Na Daya chapter 5-10

🏵MEKE FARUWA 05🏵

 Kamar wasa ya kuma tada daki ashe zai cika ne wannan karon 'yar yarinya ya dauko musu daga kauyan Turunku Mara kunya nan suka hada kai su uku suna mata habaici wai juya su kam sai zazzaga haihuwa suke, cikin ikon Allah sai ga Fatima itama ta wayi gari da ciki. Kwanci tashi har haihuwa tazo, komai na gama da ciki don kayan yara duk ita ta siya, domin da ta tambaye shi cewa yayi shi dama bai taba sayan kayan jarirai ba kuma kanta ba zai fara ba. Suko sauran kishiyoyin nata sai zundenta suke wai ba saban ba su wance anyi ciki.

Bisa ga yardar Ubangiji ta haifi'yarta ita daya kuma cikin dare, maigidan dama dakin Amarya yake, ita ce ta yanke cibi da kanta dama tana da sabuwar rezarta, sannan in ta zaga sasan Goggo sasa takan tambaye ta yanda zata yanke cibi saboda ko zata haihu cikin dare, ba zata samu mai kira mata Goggo ba. Ta nade' yarta cikin zani da ta huta ta tashi ta kwashe jinin. Da Asubahi Allah ya kara mata karfin jiki ta fito ta dora ruwan wanka, ta wanke 'yarta mai matukar kyau sunusi babban yaron maigidan nasa dan gidan Ladiyo ya leko wai in ji Goggo salame ( amaryarsu kenan) ta ce ki bata kwanon koko, ta ce babanka fa? Ya ce ta yana dakinta ta ce kaje ga kwanonin ka kai sannan ka ce babanku yazo na haihu, da murna yaron ya tafi kun San yara da dokin haihuwa, sai ko gashi ya shigo ba yabo babu fallasa fuskarshi ya dauki yarinyar ya gani ba ko addu'a ya aje ta kilama bai iya addu'ar ba ta ce don Allah ka siyo min dan kayanta mana? Ya dube ta ke Fatima dube ni ba kanki na soma haihuwa ba, bare ki min tsurfa in za ki sha kunu kisha duk sauran kunu ake dama musu.
Ta ce to yanzu wa zai je ya fado ma'yan Bauchi? Ya ce wannan kuma ya rage naki, ni dai bani da kudi haihuwar nan ma ki samu ko masarar fate in Samar miki kada ki sa rai zan yi wata karya dan bani da hali. Ta dube shi cikin takaici tare da da na sanin auranshi. Ta ce duk matan ka ka fifita su kai na, domin ganin idona kana sai musu kayan (shayi) sannan ka musu ragon suna har ma da dan dinkin suna, ban sani ba ko sun fini yi maka biyayya ne?  Tsaki yayi sannan yayi waje, tayi ta tashi wani dan saurayi jikan Goggon sasa ta mishi kwatance ya tafi Bauchi don shaida ma iyayanta.

Washe gari kanwar Umma ta biyo dan aike suka dawo ta ci gaba da kula da ita a zaman Inna hausi ta tabbatar Fatima tana matukar hakuri domin komai da kanta take saye don abincin gidan nasu baya ciyo ga Inna hausi sai daiu su yi yar miyarsu haka ake har suna tun ana gobe yan Bauchi suka zo, masara kurum ya miko ko gishiri bai bada ba ita ce ta yi komai, dangi sun hada mata shatara ta arziki, ya kuwa ta ce suna Bilkisu mai gadon zinari. Tubarkalla Masha Allah haka kowa ya ke cewa in ya ga Bilkisu shi ko ubanta ko kaza bai yanka mata ba bare rago amma ta zuba ido kuma ta bar ma Allah.

Haka Bilkisu ta taso cikin sha'awa da kuma birgewa amma gurin uwarta domin mahaifinta bai taba mata ko da wasa ba daga nesa bare ya dauke ta, a haka ta kuma samun cikin Sakina sannan Maryam sunnan Umma ne don haka suke kiran ta momy, sai Ku Asma'u lokacin tana goyon Asma'u abubuwa sun mata yawa ga yara maigidan baya biya musu bukatun 'ya'yansu cima ba dadi, in kana son ci da dan galmi sai ka bude bakin jakarka yara babu karatu su sun usima da suke maiya ya dai saka su amma ya bar iyayan da siyan takarda da biyan dan kudin jarabawa, don haka suka hana yaran zuwa makaranta kowacce ta kama Sana'a tana dora ma ya'yanta suke nan da yake son su bare Fatima wadda ita da ban za duk daya, gidan Hajara ta shiga wato aminiyarta, suka shawarta tace hajara shawara na kawo miki, ta ce ina jin ki Fatima, tace kina dai kallon rayuwar da muke yi a gidanmu. Ba cin kirki sai gasar haihuwa, to ba zan iya ba so nake don Allah ki ma Malam maigidan ki magana ya taimaka min da wani dan taimako haihuwar nan ta tsaya in samu in ji da tarbiyar wadannan ma balle ni mai'ya'ya mata ta ce kin yi tunani zan ko gaya mishi haka ko aka yi rubutu yayi mata haihuwar ta tsaya ta samu ta saka Bilkisu firamare..
🏵MEKE FARUWA 06 🏵

 Sana'o'i ta ringa yi sbulu, omo, manja,mangyada, lallai ana shan wahala da rayuwa,haka nan tayi ta kula da yaranta har suka soma tasawa. wata karamar sallah tazo nan ta shirya ita da yaranta, don zuwa bauchi, Bilkisu yarinya mai kyau da shiga zuci, lokacin shekarunta biyar, kawunta Aminu ya tafi da ita kallon hawan sallah, tana sha'awar kallon hawa ko a zariya tana son zuwa amma Mamanmu bata bari haka suke ce ma fatima, ba wanda ya burge Bilkisu gurin kallon hawan nan kamar wani dan yaron sarki ba zai fi shekara biyar ba tsaran ta kenan, an mishi nadi shima cikin wata alkyabba bayan shi runduna ce guda, yaron yana ta daga ma mutane hannu, itama sai daga hannu take tana mishi bye-bye, ai ko kullum bata da labari sai na Yarima. haka kawunta ya ce mata sunanshi har suka bar bauchi suka dawo zariya lbrin yarima take yi haka nan kuma sai ta shiga yin mafarkin yarima. kullum ta kwanta sai tace tayi mafarki sun wasa da yarima har abin ya ishi mamanmu tace kada in kuma jin zance yariman nan,
 don haka ko tayi sai tayi shiru. kowane sassa zundenta suke wai ta ki dora ma yara talla gata da ya'ya mata, in ta tashi aurar da su saga ni me zata kai ma ya'ya daki? sam wannan bai damu mamanmu ba ita dai burinta shine taga 'ya'yanta sun samu tarbiya tare da kulawa. Bilkisu yarinya ce mai tsananin hakuri da zurfin ciki, tana da kwazon karatu da son karatu, sabanin Sakina mai fada da kin raini don haka duk kishiyoyin mamanmu ta tsane su matuka, Maryam ko sai dai fushi da miskilanci. Asma'u auta itama akwai tsiwa tun tana karamarta, yanda yayyinu suk dukan Bilkisu sai dai ta yi kuka. Asma'u kam bata raga ma abokan goyonta shi yasa rigima kullum. Salame ta shiga dakin karima tana fadin ke 'yar gari king uwar mata? Me tayi? In ji karima bayan ta bada dukkan hnkalinta, Yau kuma takalma silifas sababbi ta sai musu. kan ta yi magana sai ga Ladiyo, kunga uwar mata? A gindinsu zata kare an siyo musu silifa. Karima taja tsaki ai ta haifar ma kanta wahala mata kai ta musu bauta ko gidan Miji suka je ba ka huta ba, mu ko masu mazan da farko in sun kawo karfi sai dai mu kwanta su mana su ma kannansu matan. salame ta ce ai Allah ya taimake mu da muka fara da maza. Ladiyo ta ce ni duk ba wannan ya dame ni ba, irin in ma kalli Bilkisun nan yarinya kyau tamkar aljana? salame ta ce kuma tafi sonta ba, tsorona daya kada wani mai halin ya aure t. Ladiyo tace kada nima ina wannan tunanin amma ga shawara ta rada musu wata magana a kunnuwansu, suka saki dariya tare da fadin kin kawo shawara. Bilkisu da kannanta cikin kayan islamiya suka nufi islamiyya, sai da ta raka kannanta kofar ajinsu Sakina da mami, sannan ta tafi ajinsu, duk malaman makarantar sun son Bilkisu saboda kokarinta tare da hazaka ga ladabi ga kuma tsafta duk da cewa kayan makarantar tasu sun tsufa amma tsaf suke a wanke. ta shiga suka soma karatu, basu dade ba wani malami ya shiga da wata yarinya sabuwar zuwa ce, duk ba zata fi Bilkisu ba, ta shigo tana yan kalle-kalle alamun bakunta Bilkisu ta kalle ta cike da murmushi,
🏵MEKE FARUWA 07 🏵 

 don haka sai ta je ta zauna kusa da bilkisu.  Bayan sun tashi sun fita bilkisu tace yaya sununki? Ta ce Mansura Sadik, ke fa? Ta ce ni sunana B M S, da fatan zamu zama kawaye? Mansura cikin murna ta ce. Insha Allahu. Ta debo kannanta itama da kaninta Abba ta dakko shi daga ajin da aka kaishi suka jero suna hira. Gidan su Mansura ba shi da nisa da islamiya, don haka Mansura ta roki Bilkisu ta shigo ta gaida Ummanta, jikin Bilkisu yayi sanyi da ganin daular da su Mansura suke ciki, lallai Mansura ba abokiyar yinta bace, domin an ce kwarya ta bi kwary. hajiya mero mahaifyar mansura nurse ce mahaifinta kuwa ma'aikaci ne a {G T Bank} da ke kaduna.
 makarantar bokonsu ta kudi ce mai tsada, haka ne yasa Bilkisu dan Jan jiki da Mansura, amma Mansura sai ta kara shige ma Bilkisu ta ki sai wata rana bata da lafiya don haka bata samu zuwa islamiyya ba hankalin Mansura ya tashi don haka kuwa ana tashi ta bi su Sakina don ta dubo Bilkisu. Sam Mansura bata damu da yanda taga gidan su Bilkisu ba, har ma da ta samu Mamanmu ta gama tuwo sai da taci, hakan ya sanyaya zuciyar Bilkisu don tana son Mansura musamman ma da ya ke Mansura iyayanta sun kasance yan gombe, tana ganin gombe da Bauchi kamar daya ne gunta  tana son yan Bauchi dangin uwa masu sonta, tana ganin kamar bata da masu sonta sai yan Bauchi shi yasa duk inda ta ga yan Bauchi tana girmamamasu, Mansura tana da son tuwo don haka sai ta samu gurin zuwa.

Ko Bilkisu bata nan Mansura tana zuwa gurin Mamanmu jin ta take tamkar mahifiyarta waton Ummanta suka niyan gidan sai suka tsiri sakin habaici, Bilkisu ma nan ta saki jiki da Umma Umma da Mamanmu suka zama kawaye, haka ya sosa ran su Ladiyo musamman da suka ga tana basu kayan sawa zuwa dan abin marmari.

Bilkisu tana zaune ciki wani ciyayi mai kama da cafet guri sanyi da iska yanda yake Kore fatau ya bata sha'awa ga fararan tattabaru suna tashi wasu suna sauka. Can daga nesa sosai take hango dan matashin yaron tasaranta bisa kan doki yana isowa gurinta ya tsaya cike jin kai. Yace ke wa ya kawo ki gonata? 

Ta dube shi nan ne gonarka? Kafin ya bata amsa sai ga wasu mutane su biyu suka kama mishi linzamin doki ya sauka, sannan ya isa wata kujera dake can gefe irin ta sarakannan ya zauna sai ga wasu mutane cikin jaja yan kaya sun tsaya a bayanshi, can kuma sai yace na sallame Ku. Suna tafiya ya dawo gurin Bilkisu ya zauna kusa da ita ke yar sakin wane lardi ne? Ta dube shi ba ni da alaka da sarauta. Ta bashi amsa, yace kin sanni? Ta dube shi cike da mamaki kai ba ka da gane mutane so nawa muna wasa da kai? Firgigita ta farka daga bacci yau mafarkinta ba irin na sauran ranaku ba ne, domin sauran ranakun tafi mafarkin suna wasan kwallon kafa, ko na raga koma na tebur, suna hira sosai, amma ya kan nuna bai ma Santa ba ne, tayi murmushi, tun tana yar shekara shidda take mafarkin Yarima gashi yanzun tana shekarar karshe a primary shekarar haihuwa kuwa sha daya su Bilkisu an soma zama yammata, kyanta kullum karuwa yake yi.
Hankalin mamanmu ya tashi domin ba ta da kudin da zata yi ma Bilkisu hidima dan zuwa secondary, duk da cewa ta ci domin makarantun gwamantin ma wannan zamanin sai kana da hali. Da kanta taje makarantar da Bilkisun ta ci sun mata lissafin tun daga rijista zuwa uniform da takardu dubu takwas har da dori. Hankalinta ya tashi bata da inda zata samo kudin nan, gidan hajara kawarta ta shiga don yin shawara, hajara ta bata shawarar me zai hana Bilkisu ta yi aikin gida ko na wata uku ne, in yaso sai ta shiga a zango na biyu tun da an amso form. Mamanmu jarumar uwa ce wacce samun kamarta sai an tona, tsamaranta cewa zata zamar wa ya'yanta uwa kuma uba, don haka ta ce ma hajara ni zan yi aikin da kaina wa ki ke ganin zan samu ya nemo min aiki? Hajara ta ce kada ki damu akwai mata masu hali da suke zuwa gurin malam zan dinga musu magana har a dace, shin maigidan naku zai barki?
🏵MEKE FARUWA 08 🏵 

 Ta ce tunda ba bani zai yi ba ai batun hanawa ma bata taso ba, shi fa yanda na kula koma menene kije kiyi amma kada ki tambaye shi, sukansu kishiyoyin nawa da yake sonsu baya musu komai, amma don rashin tunani suna nan suna ta zabga gasar haihuwa,yaran bacin kirki bare sutura, karatu kuwa sai dai na zagi ashar kam, kwando-kwando za ki ga dan karamin yaro yana saukewa, gaskiya 'yan gidanmu su ne suke bata ma zage zagi suna, shin haka kowane gida suke yi? Hajara tace a'a akwai dai masu yin amma ba duka ba.. Cike da farin ciki  tabar gidan hajara, ta samu Bilkisu da yan kannanta a cikin daki, tana koya musu darasin lissafi, nan ta zayyane ma Bilkisu komai, Bilki ta ce mamanmu ki bari ni nayi aikin in an samu, ta ce a'a nafi soe ni in yi bana son kije ki bata ma masu gidan har su sallame ki, bukatarmu ya zama bata biya ba. tace mamanmu amma kinsan bana fada ko? tace na sani maigado, amma ki bari sai dai an samu din kisan ke yarinya ce ba kowane abu ne zaki iya yin shi ba. Sallamar Mansura ta katse su, suka amsa ta shigo kusa da mamanmu ta zauna sannan tce mamanmu ina kwana? Suja gaisa ta dubi Bilkisu tace "Bily ya dai, yaushe zaki fara shiga school ni dai on monday zan fara zuwa. Bilki tace ni kam ba rana Mansu, kila ma sai second term. Mansura tace akan me? Tace kudi, mamanmu tace kin san ko mai yanzu sai da kudi ana cewa ne dai makarantar gwamnati amma suma duk shegiyar darin ce ga kudin motan zuwa makaranta kullum mansura tace bari Abbanmu yazo week end zan gaya masa. Bilki har suna hada baki da mamanmu, a'a kar ki yi masa magana shima yana ji da nasa iyalin. Mansura tayi shiru, amma a ranta ta raya sai ta fada mashi... Haka kuwa yana dawowa ta gaya mishi, ya tambaye ta ko njawa suke nema? Ta ce ya basu kowanne ita dai bata sani ba, kuma ta san ko ta tambaye su ba zasu fada ba. Dubu goma ya bata yace, gashi ki basu." sai da ta kai kudin mamanmu da yaranta suka je suyi godiya,Bilki kuwa sai da tayi kukan murna, sannan tana ta mamakin dama da gaske ne akwai iyaye masu yiwa 'ya'yansu hidima? Ba sabanin iyayansu mata da wahala?  Cikin nasara ta shiga j.s.1 mansura kullum in za su je makaranta sai ta saka direbansu ya biyo sun dauki Bily, sunan da ta ke kiran bilkisu kenan, ita kuma Bilki tace  Mansu, wani abin da yake kara ba Bilkisu mamaki shi ne, yanda mafarkin  Yarima ke kara yawaita a gare ta, ko gyangyadi take sai ta yi bare barcin dare. saboda sabon da suka yi har ta saka mishi Yarima aboki, shi ko yana kiranta Beauty, tana son sanar da mamanmu amma tasan mamanmu zata ce shirme ne, shi yasa take bar ma cikinta don ko mansu bata taba ba wa lbri ba. cikin haka hajara tazo ta ce, an samu aiki. Mamanmu tace ai ko zan yi,
🏵MEKE FARUWA 09 🏵 

Suka je gidan hajara inda hajiyar da za a yiwa aikin take jiransu.Bayan sun gaisa tadubi mamanmu tayaba da tsaftarta don haka tace girki nake so zaki iya? Mamanmu tace me zai hana.Nan suka sasanta ita da hajiya kilishi, gidanta na nan tudun wada, sun sasanta kan dubu uku, kuma za'a dinga zuwa ana daukarta haka nan za'a dawo da ita ko da ta samu maigidan nasu da batun sai yace,shi ina ruwan shi,ta dai sani dole ran girkinta tazo shima ta mishi,dama tasan haka zai ce,tunda shi dama baya son ma mace tace ko da bani kudin kamu,wani lokaci takan zauna tana tunani, anya maigidansu yana son lahirarshi ta mishi kyau?In'yan abinshi suja motsa haka zai je ya nado tsiranshi yazo ya zauna gaban'ya'yanshi yana ci ba zai sammusu ba in ma yaga suna kallonshi sai yace kai daina kallona ka da ka saka ni in kware.Ko ya fita bakin titi da yamma ya sayi doyarshi da kwai ya zauna yana ci in an ce yara suzo suce yaba da kudin cefane sai yace kai zauna nan kayi wasan ka shareta,kuma fa in yaron nan ya zauna haka zai cinye ya hana yaron, halin wannan mutum sai shi hakika baici sunnanshi ba.  Cikin sa'a Mamanmu ta soma aiki tana tafiya da safe in yaranta sun tafi makaranta da sha biyu suke maidota gida, in ta gama musu abincin rana domin tana son ta zo ta sallam yaranta. hajiya kilishi kan ce Dibar musu ki kai musu. Sannan karfe hudu zata koma tayi na dare, in ranar girkinta ne kuma sai shida take tafiya don ta samu ta gama na gida. Su kam su ladiyo, nan suka soma nuna hassada tare da canza mata suna daga uwar mata zuwa boyi. Su yi ta mata habaici tare da maganganu marasa dadi, kafin wani lokaci mamanmu da 'ya'yanta sun canza,sunyi kyau, saboda cima ta canza in ta kawo abincin takan dibar musu ta mika ma ladiyo tace su ba wa yara, suna zaginta suna komai haka zaki ga suna kason su sai kace daukin nama su da ya'yan suna ci tandar harshe. Hajiya kilishi tana da yara mata kusan sa'annin su Bilkisu don haka suna samun kaya. Rayuwa dai ta canza yanzu har da sabulu mai kamshi suke wanka.  Cikin haka suka shiga J.S 2 lokacin alamun girma ya soma shigar ma Bilkisu, kyanta ya soma bayyana, duk layin kowa sai zancenta yake yi, sun kuma kara shakuwa da mansura duk in da kaga zara za ka ga wata.Bilkisu tana da kulafucin karatu don haka bata da lokacin komai sai na karatu. Azumi ya matso gashi, lokacin ana fama da rashin kudi a gari, 'yar doyar da maigidan ya kawo buhu daya ce, nan ya kasata gida hudu yace kowa ya kwasa sannan kada wacce tai mishi zancan geron kunu domin ba shi dashi, cikin haka Azumi ya kama. Saboda rashin hankalin su ladiyo sai suka ce ma maigidan su fa kowa tayi girkinta kenan suna kyashin taimakon juna, maigida yace wannan lalurarsu. Mamanmu ta ji dadin hakan domin ya'yanta hudu ne,kuma dama aiki yana mata yawa,ranar girkinta yanzu kam hajiya kilishi tace ki dinga hada girkin tare da yaranki,dama ga alale da kunun tsamiya na sadaka da ake yi ana bai wa al'ummar Annabi sai kurum ta huta da yin girki biyu,in ma dakinta yake sai ta dibi nashi cikin kwano samira da kunu a kofi. Bilkisu taje ta amso, wataran ta roki direban ya kawo nan zaka ga malam maman an baza tabarma tsakar gida ana kwasar gara, cefanan wani kai ka kasa, haka matan ke ce mishi,in sunga yana rawar kan cin abinci ran girkin mamanmu,haka nan mijinta da yayi rabon kayan azumi shinkafa, masara,gero,da kuma suga sai daya ba mamanmu kowanne buhu,jikin kishiyoyinta ya dauki bari bakin cikinsu ya kasa boyuwa ita kam kowa sai da ta dibar mishi har 'yan sauran sassan da su rukarta su goggon sasa tare da matan yayyin maigidan nasu da na kannai. Wato mamanmu mace ce mai rama alkairi ga duk wanda ya mata sharri, tana da matukar hakuri tare da sanin ya kamata, in ban da haka yanda kishiyoyin nan nata suke mata kai har shi kanshi maigidan yafi mata wulakanci akan sauran kishiyoyin nata, amma hakan bai sa tayi tunanin cin zarafinshi ko kishiyoyin ta ba sai ma kyautata musun da take yi, shi yasa kullum cikin ci gaba take. Hatta abincin sadaka ko nata in tayi sai ta basu..

MEKE FARUWA Littafi Na Daya

MEKE FARUWA 01
Yana kwance cikin tafkeken bahon wankan da ke cikin tsfkeken bayin, Sam bai yi kama da bayi ba, domin yana da girma kwarai. Bahon kato ne haka nan daga inda bahon kana iya kallon TV manne jikin bango can daga nesa kadan ga gurin da zaka zauna don yin bahaya (toilet) tsararre ne mai tsafta. 
Kwance cikin baho Modibbo ne, daga in da yake cikin bahon da ya cika da ruwan dumi da kuma ruwan sabulu mai shegen kamshi yake canza tashar da yake kallo zuwa (CNN) daga inda yake yana jiyo karan kawankawasa  kofar bayin. Shin wanene? Ya tambayi kanshi amma ci gaba yayi da kallonshi. Da ya tuna duk Wanda ya matsu ya jira shi kusan rabin sa'a sannan ya soma cuda jikinshi, ya cire abin da ya toshe rariyar da ruwan ya tsiyaye sannan ya kunna wani dake zubowa daga inda aka rataye su ya rufa a jikinshi sannan ya dauki karami yana goge sumar kanshi. Bayan yazura lallausan silifas a kafarshi zama yayi kan wata kujera duk dai nan cikin bayin ya shafe jikinshi da mai mai kamashi tare da turaruka ya gyara sumarshi tare da shafa mata nata kalolin.
🏵MEKE FARUWA 02 🏵

 Modibbo yana kashe ma kanshi kudi fiye da zaton mai tunani,mikewa yayi cikin tafiyarshi ta kasaita ya nufi dakin barcinshi don saka tufafi ya kalli kofar da zata kaishi falo sai ya tuna ana jiranshi, din taski yaja sannan ya rufe kofar (bedroom) din shi bayan ya shige tare da fadin ko ma waye zai tafi ne don yanzun lokacinan na kar2 ne. Shirayawa yayi cikin wandon {jeans blue} da rigarsahi mai dogon hannu ya isa kan durowa ya kwashi takardu tare da wayoyinshi ya zuba su cikin aljihu, takalmanshi sawu ciki ne ya saka sannan ya fita.
  Vicky ce zaune a falon tana jiranshi,ji yayi tamkar bai ganta ba duk da tsananin son da yake yi mata. Ya nufi hanyar fita, ta taso da sauri tana kiran shi. 

Darling prince D P
Ci gaba yayi da tafiya, ta soma gudun sassarfa ta cinma shi ta dafa kafadarshi tana cewa cikin turanci. 
Duban ta yayi tamkar ba zai magana ba sannan yace amma kin yi saurin hucowa. Ya taba baki" ina zaton kin manta ni wanene shi yasa kike yi min fushi, bani da lokacin lallashin ya mace duk da son da nake musu. Ki gane bani Yarima Modibbo ke bin mata ba, ni suke bi. Je ki ci gaba da fushi dan kin ganni da wata. " yaci gaba da tafiya yana sake fadin Yanzu lokacin kar2 ne ba na surutu ba. 

Ta tsaya ranta a bace,hawaye ya soma zubo mata tana tunanin yaushe ne zata daina kuka saboda prince? Yaron da take matukar so, yaron da mata suke rububinshi, yaron da yake ma mata jan-aji, yaro mai kyau da kwarjini, ta zube ta soma kuka. 
 Kafin ke dubin ki sun yi Vicky . 
Yarima Al-amin kenan. Kenan dan sarki Ismail jikan Abdullahi mai mulkin yankin Bauchi. Matashin yaro dan shekara ashirin da biyu  Wanda aka fi sani da YARIMA MODIBBO A malesiya gurin kar2 ake CE mi shi prince

A ZARIA FA? 
 
Katon gida ne ginin kasa mai dauke da sassa kusan goma sha biyu, gida ne ginin kasa tun na da wato ginin gargajiya. Kafatanin 'yan gidan dangin juna ne in ka dauke Fatima'yar mutanen Bauchi da aure ya kawo ta gidan. Yanzun da haka fatimar ce zaune tana tuka tuwon dawa, Bilkisu ta yi sallama ta shigo jikinta sanye da atamfa java, ta rataya jaka kana ganinta kasan daga makaranta take. Bilkisu kyakkyawa ce ta bugawa a Mujalla, domin idan har za'a zuba gasar kyau ta shiga ciki babu abin da zai hana ta lashe gasar 'yar kimanin shekara ashirin da biyu CE. Ta isa gurin mahaifyarta Fatima tana fadin.

Mamarmu sannu da gida Ta dube tace da kulawa duk da kasancewarta'yar fari ta ce "yauwa sannu maigado. { shi ne sunan da ake kiranta da shi } ma'ana mai gadon zinar. Kirarin maisuna Bilkisu. 
   Yau kin dawo da wuri. Ta ce " Eh, Mamarmu wata kawar mu muka je dubawa da tuni na dawo. Ta ce Allah sarki, bata da lafiya ne? 
 Zazzabin cizon sauro ne, nan sabon gari suke. 
 Allah ya bata lafiya. In ji mamar. Amin . Bilkisu ta amsa. Sannan ta nufi dakin mamansu duk da gajiyar dake tattare da ita sai da ta share dakin fes tare da gyara shi. Sannan ta fito ta share tsakar gidan duk da cewa ba'a siminte yake ba, yakan ba da sha'awa in an share . 

Asma'u Auta ta shigo da sallama, ta dawo daga Islamiyya tace, Sannu Mamarmu, sannu Aunty Maigado. Bilkisu ta harare ta da sauri ta gano laifinta ta ce, Na manta ne, yi hakuri. Tana yar dariya . Bilkisu ta ce ban son Aunty ki ce min Bilkisu kawai don bana son maigado . Ranar da ki ka kara fada sai na fasa miki baki. Mama ma ta ce. To ai sai a hankali zata saba, mu dai ai ba yanda za ai damu. 
🏵MEKE FARUWA 03🏵
Ta dubi Asma'u. 
Auta amso min kwanukan mutanan gidannan in kwashe tuwon nan. Dakuna uku duk da na su hudu sashen Babansu malam mamman kenan matanshi hudu ya'aya ashirin da takwas, don haka kwanukan da Asma'u ta baje gaban Maman mu sai ke ce za'a kaima gidajan layin gaba daya ne, yawancin kwanukan duk sunyi tsatsa da kuma lamba, haka Mamanmu ta ci gaba da kwashe tuwon nan tana zuba ma kowane. Bilkisu ta fito daga daki tana cewa, Mamanmu bari in debo ruwa in kin gama sai na dora ina son na yi wanka. 
 
Tace, ai fa ke kam ko kwado ya San da zamanki gurin wanks. Dariya tayi sannan ta dauki bokiti zuwa gurin rijiya. Kananan yara sun kai hudu suna wasa da kasa a bakin rijiyar, maza uku mace daya macen mai suna Safiya tana zaune tsakiyar tabon da suka kwaba, rigarta duk koko haka nan fuskarta, kanta rabi a tsefe rabi da kitso. Tsaki Bilkisu taja sannan ta ce da su. Kai Ku ta shi a nan kazaman yara kawai."  Bala dan babba a cikin su ya kalle ta. 
To ina ruwanki dama za ki ce mu ta shi? 
Ta samu kanshi ta dan buga dai dai da shigowar mahaifinsu Malam Mamman. Yace ke ke ke kar ki sake ki duke shi, ki shafa mishi bakin jininki
  Ta dakata. Me yayi miki? Ko zalinci da mugun Abu za ki nakasa min da namiji gashi ke uwarki bata iya haihuwar ya'ya maza ba. Ya ja tsaki kai Bala. { hahahah wai bala dama bala sunane?} Idi, kuzo muje ciki domin zata iya jefa Ku cikin rijiyar nan yan ubanci ba karya ba ne.  Allah ya kyau ta. 
Bilkisu hawaye suka zubo mata, ita dai tana matukar mamakin irin tasanar da dukkan dangin mahaifinta 'yan dai-dai-ku suke yi mata ta dibo ruwan ta dawo, yanda taga fuskar Mamanmu tasan cewa ta ji duk me baba yace mata, don haka ta ce kiyi hakuri Mai gado wata rana sai labari .
Da daddare kwance take kan gadonta, gefenta Asma'u ce tana ta shara barcinta, ita kam ta zurfafa cikin tunanin cukurdaddan al'amarinta, kullum tana tambayar kanta shin me ke faruwa da ita ne? Tana da kyau na gani afada, tana da hankali ta sani domin mutane suna fada, tana da ilimi duka biyu wato islama da na boko. Natsuwa da kamun kai kuwa ba a magana, amma me ya hana ta burge maza? Me yasa ba ta da saurayi?me ya hana wani yace yana son ta? Kuka ya kufce mata Wanda ya zama dan kullum. A fili tace. Meke faruwa ne da nine? Wa zai bani amasar tambayata?  Shin ko Ubangiji bai kaddaro ni cikin wadanda zasu yi aure ba ne? Allah kai kadai ne mafi sani......... Ta daga hannuwanta  Ya Allah Ya Ubangiji halitta kai ne majibancin al'amurana, kafi ni sanin halin da nake ciki, Allah ka zaba min mafi alkairi. Ta maida kai ta kwanta ta soma tuno ita wacece? 
 Uhm sai an jima.

 GIDAN MARINA, shi ne sunan da ake kiran gidanmu a unguwarmu, wato Ojo saboda 'yan gidanmu ita ce sana'an da suka gada daga kakanninsu, kuma ita ce har yau yayanmu suke yinta wato rini. Gidanmu katon gida ne mai dauke da sassa sama da goma. Asalin maigidan shi ne Malam salisu, shi ne mahaifin su Babanmu. Yana da mata hudu 'ya'yanshi talatin da bakwai maza guda goma sha biyar sauran duk mata ne, mahaifinmu yana cikin ya'yan Goggo Amarya shi ne da na uku a gurin ta yana bin mata biyu, kakanmu malam salisu mai rini mutumin kirki da sanin ya kamata, ya rasu tuntuni lokacin ma ba'a haife ni ba, uwargida ma lantana Allah ya yi mata rasuwa, yanzu saura mata uku. Tun rasuwar malam salisu gidan ya lalace rigingimu tare da matsaloli sukayi ma gidan yawa. Gidanmu ba'a cika auran bare ba sai dai dan wannan daki ya auri 'yar wancan daki, suma su ja na su sasan ko kuma cikin dangi na wani gu ya auro kuma dangi na wata unguwar ya auri yar gun, haka suka ke yi har zuwa kan mahaifinmu, wanda suka yi bikin wani abokinsu aka kawo Amarya daga Bauchi, cikin kawayan Amarya idon shi ya kyallo Fatima yar mutanan Bauchi daya daga cikin kawayan Amarya, nan ya birkice kun san bazazzagi da mace. Nan fa ya shiga zarya tsakinin Bauchi da zariya, Fati ta yarda itama tana son Muhammadu, wanda yan gidan basu goyi baya ba, saboda tuni yasan da hatun ladiyo yar kanin mahaifinshi baba isa dake jushi, hakan yasa duk yan gidan kin amin cewa da batun har da mahaifiyarshi goggo Amarya .
 
Goggonsa ce kurum ta ce ai hakuri ba a san rabo ba, tasa'ya'yanta su shige mishi gaba gurin neman auran, bayan kai-kawo aka biya sadaki sai bikin, ya gina sanshi kamar sauran'yan gidan ginin kasa ciki da falo, aka kawo Fatima dakinta, zaman nasu ba laifi sai dai bata jin dadi'yan gidan sai Goggon sa kurum.
 🏵MEKE FARUWA 04🏵

 Bayan'yan watanni sai rayuwa ta canza tun da gara ta kare shi kenan mataloli suka kunno kai cikin zaman nasu, farko ya sakar mata sayan su sabulu, man shafawa, daga baya suturar a shekara dama yake mata itama ya daina, daga baya ma sai ya zama abinci in ya kawo masara ko dawa ko kuma doya to batun cefane can ta gane, cikin haka dangi suka soma tsegumin shekara biyu babu haihuwa gaskiya sai dai ya sake aure, haka ce ta faru. Ladiyo tana jiranshi nan ko aka soma shirin biki Fatima ta zuba ido domin sabon shafi ne na wulakanci ya bude tsakaninta da dangin mijin da kuma shi kanshi maigidan saukin ta daya goggon sasa tana yin kuli to sai tana bata mirji da suya tana biyanta a haka Goggo ladiyo ta shigo cike da gadara da jin kai har zama yayi zama kafin wata biyu ladiyo ciki ya bayyana. 

 Nan dangin miji suka sakota gaba ko yaransu suka hana ta aika, sukan ce ta abr musu'ya'yansu in taga dama ta haifi nata, ya zama sai dai in tana son aike sai taje, ko kuma ta fita makota ta aika yaransu. Duk wannan ba shi ne tashin hankalinta ba irin yanda Ladiyo ta tsiro tsirfar bata son warin tuyar kuli kuma in taga tunkuzar kuli tana sakata yin amai, kenan'yar sana'ar tata ta barta a halin da ita ne take samu tana rufa ma kanta asiri.  
 Tabbbas nufin Ladiyo ta samu ta raba ta da sana'arta, maigidan kam ya ce baya son ya kuma ganin kuli ko tunkuza, ta ce amma kasan cewar da wannan sana'ar na dogara ko?  Nan take ya fusato, kenan ke kike ci da kanki? Ta ce menene marabar dambe da fada? In ka kawo min hatsi ko doya shi kenan, ba kudin cefane ba na nika ko na ice, sabulu, man shafawa duk a jikina suke fita, ya ce to koma menene dai a daina min kuli, tace gaskiya ba zata yiwu ba, ni kenan kullum sai dai dangi su taimaka min? Ya ce kanki aka soma?  ai ba kanki mata suka fara cefane ba, don haka ki canza sana'a, ta ce amma ai ita Ladiyo kana bata ba dan baka dashi ba ne kake hana ni, saboda haka yanzun na soma yin kuli in ba'a so in yi sai a tsare min komai, " ya fita tare da fadin To bismilla, kiyi ki gani, haka ko washegari ta amso aikinta ta shiga yi,  Ladiyo ta fito shi ne kike kulin dan ki ga bana son warin so kike cikina ya zube ne tun da ke ba ki iya samun cikin ko? Bata tanka ba ta ci gaba da aikinta, makira mijin na shigowa da gudu ta shige daki ta hau gado tana ta burgima tare da kakarin amai. Yana ko karasowa ya shiga masifa har da zaginta, a karshe ma dukanta yaso yayi ta shige daki. Washe gari kam ta ce ta gaji gida zata tun da tana da gatanta hakuri kuma ba hauka ba ne. Wannan tsiya, yau miji ya maka gobe mutan gida, uwarmiji sai ta shigo har sasansu ta zage ta tas tana cikin wannan tunanin tana hada kaya, taji muryar Goggo Amarya.
 Ina kike 'yar mulki da iko da an ce ki daina aikin kuli saboda mai cikin haihuwa ke naki cikin ban da kashi ba ya iya daukar komai shi ne za ki bar gidan, itama mai baki aikin ai munafunci ne ga mata da yawa kowane sashe ta mika aiki ai yi zasu yi amma dan gulma ta fi son ta ba ki shi yasa bata ciniki to mai farar kafa ta taba ba dole yayi kwantai ba?

 Fatima kam shiru ta yi tamkar bata nan, Goggo ta gama masifarta ta fita,itama ta dauko kayanta da saka su cikin garin yayi zafi ta fita a waje yayyan maigidan ne su biyu sani da Rabi'u suka ce ina za ki? Ta ce zan yi tafiya ne, suka ce in dai yaji ne kiyi hakuri, ta ce kai ita ta gaji gara taje garin su. 

Daf da magriba ta iso Bauchi, sanda ta shiga gidan su mahaifiyarta tana alwala ta ce lafiya kuwa? Murmushi taye tare da fadin lafiya kalau bayan sun yi sallah sun ci abinci nan ta shiga zayyano ma Umma abin da ya faru tare da halin da take ciki. Umma ta ce bari Malam ya shigo. 

Iyayanta suna da mutunci tare da sanin ya kamata, suna son Fatima sosai, saboda ita kadai ce ya mace a cikin 'ya'yansu maza guda biyu. Aminu da Abubakar wadanda suke kasuwancinsu a nan babbar kasuwar Bauchi, kuma suna da iyalansu suna matukar kula da iyayansu da kuma Fatima. 

Sun hada mahaifinsu da yayyanta sun yanke shawarar in yazo biko za'a ja mishi kunne sannan ta koma, ta ce ita in so samu ne a raba Auren amma sai mahaifinta ya ce ba zai yiwu su kashe mata aure ba, ta je ta ci gaba da hakuri. Satin ta daya sannan 'yan uwanshi suka zo shima sakamakon yanda 'yan uwanshi suka matsa mishi da magana har da makota sannan ya yarda yazo bikon tare da'yan uwan nashi. 
An ja mishi kunne 'yan uwanta sun hada mata jari tare da dunkuna sun ce taje ta sayi fridge ko ruwan sanyi ne tana saidawa,  ta dawo dakinta ta ci gaba da hakuri tare da yan sana'o'inta haka nan ta sai fridge din tana kuma samun alhairi haka Ladiyo ta haihu suka yi ta rawar Kansu har aka yi suna hankalinta kawance, tunda tana sana'arta. Cikin watan ya sake ta da wani dakin yana gamawa ya rigimo Auren karima bazawara ce daga unguwan kaura aka sha biki itama tabi sahun yin cefane da kanta, wankau ta ke yi, shekarara danta sunusi daya ta kuma samun ciki sai fa suka soma gasar haihuwa ita da karima Fatima ta da dai zuba ido ya'yansu maza suke Haifa.

Yadda Zaka sayi data mafi sauki a layin Ka na MTN 10Mb for #2

Yadda Zaka sayi data mafi sauki a layin Ka na MTN
Akan Naira biyu 2 zaka iya Sayan 10mb
Abun Babu wahala Sai kai dial na Wanan code din zasu baka zabi Kamar yadda yake a hoton nan

KA KARANTA A NATSE

KA KARANTA ANATSE.
Misali.
Wata rana wani Mutum ya fita domin za'gayawa cikin gari.
Babu zato babu tsamma'ni sai yaga wata qosash'shiyar sa'niya. Sannan kuma hantsar sa'niyar kamar zata fashe. Saboda yawan nonon da yake cikin hantsar.
A lokacin da wannan bawan Allah yaga sa'niyar nan. Sai ya tina da sa'niyar maqwabcinsa wacce y'ar qarama ce. Kuma a yunwace take.
Ko zancen sa'mun nono a jikinta ba ayi. Kuma ga'shi maqwacin nasa yanada y'ay'a bakwai kuma duk mata. Kuma maqwabcin talaka ne futuk.
Don haka sai wannan bawan Allah ya siyi wannan sa'niyar. Ya baiwa maqwacinsa ita kyauta.
Yayi masa kyautar sa'niyar ne. Saboda Allah s.w.t yace:‎

“ﻟﻦ ﺗﻨﺎﻟﻮﺍ ﺍﻟﺒﺮ‎ ‎ﺣﺘﻰ ﺗﻨﻔﻘﻮﺍ ﻣﻤﺎ ﺗﺤﺒﻮﻥ.”‏
A lokacin da yaba maqwabcinsa kyautar sa'niyar. Sai maqwabcin yaita godiya kamar bazai daina godiyar ba.
Saboda farin ciki.
Bayan wasu watanni sai wannan bawan Allah ya fita fatauci shi da y'ay'ansa.
Suna cikin tafiya a cikin saha'ra. Sai qishin ruwa ta riqa da'mun wannan bawan Allah. Ga'shi kuma ruawansu ya qa're. Saboda y'ay'ansa sun shanye ruwan duka
suna na cikin tafiya a sahara sai sukaga wani qa'ton rami mai matuqar fa'd'i. Da yalwa
bawan Allahn ya kalli ramin yaga. Akwai ciyayi a cikin ra'min. Saboda haka lallai-lallai za'a iya sa'mun ruwa a cikin ra'min.
Don haka sai yacema y'ay'ansa. Su jirashi a waje. Shi zai shiga cikin ra'min domin yasha ruwa.
Y'ay'ansa suka tsaya a waje. Shikuma ya shiga cikin ramin.
Alokacin da yashiga cikin ramin. Yasha ruwa. Sai hanyar fitowa ta 6ace masa. Don haka sai yaita bula'yi a cikin ramin. Amma ya rasa hanyar fita.
Y'ay'ansa suka tsaya a waje sunata jiran fitowarsa. Amma sai sukaji shiru. Haka sukai ta jira. Hardai suka yanke qauna ga fitowarsa. Domin a tinaninsu ya mutu. Ko kuma wani miciji ya sa'reshi.
Don haka sai y'ay'an nasa suka fara tinanin ga'do.
Nanfa y'ay'an sukayi sauri suka koma gida.
Haka suka riqa tattaro dukiyar mahaifinsu zasu rabata ga'do. Suna cikin tattaro dukiyar ne. Sai 1 daga cikinsu ya tina musu da sa'niyar da mahaifinsu ya bayar kyauta ga maqwabcinsu.
Don haka sai sukaje wajen maqwabcin domin su kar6o sa'niyarsu. A tinaninsu ta zama tasu.
Sai maqwabcin yace musu: ai mahaifinku yayi mini kyautar sa'niyar.
Kuma ni da y'ay'ana muna amfani da sa'niyar.
Sai sukace masa ka da'wo mana da sa'niyarmu. Zamu baka wani d'an qaramin raqumi. A maimakon saniyar. In kuma ba haka ba. To zamu kwa'ce sa'niyarmu. Da qarfin tsiya. Kuma bazamu baka komai ba
Sai maqwabcin yace: zan kai qa'rarku. Wajen mahaifinku.
Cikin izgili y'ay'an sukace: kakai qararmu gurin ko waye. Amma baba ai ya mutu.
Cikin firgici ya tambayesu: ya akayi ya mutu. Ban sani ba?
Sai sukace: wani rami ya shiga a cikin sahara. Kuma ya kasa fitowa.
Sai maqwbcin yace: ku nuna mini inda ramin yake. Sai ku d'auki sanirku. Kuma bana buqatar ku bani wani abu.
Sai suka amince. Kuma suka kwatanta masa inda ramin yake.
Da maqwabcin ya isa inda qa'ton ramin yake. Sai ya kunna wuta ya riqe a hannunsa. Sannan ya shiga Cikin ramin.
Haka yaita yawo a cikin duhun ra'min. Hardai yaji ya fara jiyo nishin wani abu. Ahankali-ahankali. Sai doshi wajen ya shafa yaji ya ta6o mutum.
Sai ya sa6o mutumin a kafad'a ya fito dashi waje. Ya bashi ruwa.
Sannan ya d'aukeshi yakaishi gidansa. Haka ya riqa jinyarsa. Har ya murmure.
Duk wannan abu da yake fa'ruwa. Y'ay'an mutumin basu saniba.
A lokacinda ya murmure sai maqwbcinsa yazo wajensa Cikin ma'maki ya tambayeshi:
YAYA AKAYI HAR KA KWASHE SA'TI 1 ACIKIN RAMI. Kuma kana ra'ye?
Sai yace: zan gaya maka. Wani labari mai ban ma'maki.
Ai lokacin da nashiga cikin ramin. Sai nasha ruwa na qoshi. Sannan na riqa qoqarin fitowa. Amma sai na ka'sa fitowa. Saboda hanya ta 6ace mini.
Haka na riqa shan ruwa acikin ramin. Har na kwa'she kwanaki 3. Sai yuwa ta riqa da'muna.
Saboda tsananin yunwa sai na fa'd'i na sallama cewa mutuwa zanyi. Babu zato babu tsammani kawai sai naji nono yana zubowa ba'kina. Daga wata qa'tuwar qwarya. A cikin duhu.
Haka Wannan qwaryar nono ta riqa zuwa wajenane sau 3. A kullum.
Amma kwana 2. Kawai kwaryar tayi tana zuwa. Kawai sai naga ta daina zuwa. Ni kuma bansan dalilin daina zuwanta ba.
Sai maqwabcin ya gaya masa dalilin daina zuwanta.
Yace masa: ai y'ay'anka ne. Suka kar6e. Saniyar da kabani.
To nidai ina tinanin wannan shine dalilin daina zuwan wannan qwaryar nono.
Ya Allah s.w.t ka bamu damar yin kyautuka domin kai. Badon wani yasan muna'yi ba.
Ya Allah s.w.t ka agaza mana.

Kaddara ta chapter 5

KADDARA TA Chapter 5

Tana zaune a parlour waya ce a hannun ta tana
dannawa,saukowa da Anti farida tayi cikin shiri hannun ta
riqe dana su Fudel da Fausam kamar wasu twins dan
Fausam ne first born se Fudel tazarar 1 year ne a tsakanin
su shiyasa idan ka gansu zaka ce kansu daya shekarar
Fausam 5 Fudel kuma 4.
Kallon su take tana murmushi ta ajiye wayar ta a gefe
sannan ta daga Fudel sama suna dariya sannan ta ajiye
shi tana fadin
"Anti farida se tafiya kenan?"
Gyara mayafin ta take tace
"Tafiya za muyi se ki mana gadin gidan"
Dariya suka yi har mota ta raka su dan ita ce zata yi
driving.
Zulfa'u ta dan bata fuska tana fadin
"Anti ni kadai zan zauna?"
Hararar ta tayi tana fadin
"Me zai cinye ki a gidan?"
Dariya tayi sannan tace
"Salim ma zan kira kwana biyu bai zo ba"
Riqe baki Anti farida tayi tana fadin
"Lallai kam,ki ce masa munyi hannun riga tunda kwana
biyu ya manta da mu"
Dariya kawai tayi hade da daga musu hannu har motar ta
fice sannan ta koma ciki ta kira Salim.
30 mins ya kira ta yace yazo.
Daukar vail dinta tayi dan wasu riga ce iya gwiwar ta me
dugun hannu kalar black and white se kuma straight skirt
ko kwalliya bata yi ba ta dan fesa turare sannan ta fito.
Motar sa qirarrar corolla kalar fara ce yayi parking,tunda
ta fito ta hango wadanan zaune can zaune kan kujera se
table da wasu abubuwa akai ko ba'a fada mata ba tasan
taba suke sha.
Su 5 se dariya suke suna tadi da alama yanayin yana
musu dadi,kallo daya ta musu ta dauke kai hade da jan
tsaki.
Gannin ta fito yasa Salim fitowa daga motar ya jingina
jikin motar yayi folding arms dinsa yana binta da kallo.
Salim yana da kyau dan fari ne se dai ba sosai ba yana da
tsayi kuma ba kato bane dan siriri ne yana da son tara
suma se dai ba sosai ba,yayi kyau cikin qanan kayan da
ya saka sun amshe shi matuqa.
Saukar da kanta qasa tayi bayan ta iso inda yake gannin
irin kallon da yake mata.
"Ka shigo ciki mana"
Ta fada tana kallon sa
"A'ah ba se na shiga ba bana so mu hadu da Anti farida
na mata laifi"
Dan murmushi tayi tana gyara zaman eyeglasses dinta
sannan tace
"Ai kowa tana nan tana jiran ka da irin punishment din da
zata baka"
Dariya suka yi wanda a lokacin Zulfa'u ta dago cikin eye
glasses dinta suka hada ido da daya daga cikin su
Christoph,dan ko ba'a fada mata ba tasan maganar su
suke gannin irin kallon da suke musu,dauke kai tayi suka
cigaba da magana da Salim.
"Guy who're does?your neighbours huh?"
Inji Daniel daya dauke cup yana shan ruwa hade da kallon
Christoph dake danna waya wanda hankalin sa ma baya
inda suke.Se a lokacin ya dago ya kalle su Zulfa'u dake
hirar su hankali kwance,lokaci daya ya dauke kai hade da
fadin
"Maybe"
Favour dake shan cigarette ya dan yi dariya yana fadin
"Wannan small pikin hira ta fito"
Tabe baki Christoph yayi yana fadin
"Child abuse"
Dariya suka sa banda Christoph daya hade rai Wale dake
buga whot shida Mercy yace
"Ina ruwanka dasu hadda wani wannan child abuse ne?are
u jelouse?"
Wani kallo yayi masa wanda yasa suka qara shekewa da
wata dariyar,ya wani bata fuska yana fadin
"This girl is not my type she's a muzlim and u know i don't
like fat girls,besides i don't like girls who where glasses"
Mercy ya dan kalli Zulfa'u na tsawan wasu seconds din
kana yace
"Buh dude i think she's ok the way she's every thing is
well backege"
Dariya sosai suka sa hadda tafawa da Wale wanda hakan
se daya sa Christoph murmusawa
Daniel yadan dafa kafadar Christoph yana fadin
"Wai kasanta ne?"
Girgiza kai yayi ya cigaba da danna wayar sa Daniel yadan
yi shiru kamar yana son cewa wani abu daga baya kuma
ya yi shiru kawai.
Tashi Mercy yayi yana gyara rigar shi wacca take armless
duk muscles dinta sun fito yana binsu da kallo hade da
nunu wrist watch din dake maqale a hannun nasa Rolex
yace
"Guys we're wasting time by 6:00 we should be at that
place and now it almost 5:40 we're running out of time"
Nan da nan suka miqe kowa ya dauki abun sa me amfani
kana Wale ya kalli Christoph da bashi da niyyar tashi yace
"Chriss are u not coming?"
Girgiza kai yayi yana fadin
"No i'm not coming we meet tomorrow"
Tashi yayi har inda car dinsu tayi parking ya raka su har
sun shiga motar su gate man ya bude Dan ya leqo ta
window motar ya dan daga murya yana fadin
"Jay about that babe Angelina"
Dariya Christoph yayi yana fadin
"We talk about that shit tomorrow"
Daria suka yi yana daga musu hannu har motar su ta
fice,kallon su Zulfa'u tayi tana mamakin su dan duk cikin
su ba me shigar kirki kamar wasu mata daga me sarqa se
me dankunne.
Komawa yayi ya zauna ya cigaba da abinda yake yi,wani
dan yaro ne ya fito daga flat din wanda bazai wuce su
Fudel a shekaru ba yana fadin
"Uncle Jay! Uncle Jay!"
Ya fada kansa,daga shi yayi yana juya shi hade da fadin
"Yesss my boi"
Shi kuma se bingira dariya yake ya saba shi a kafada suka
shige site din.
Har Salim ya tafi tunanin su Christoph bai bar brain dinta
ba.

Kaddara ta chapter 4

KADDARA TA Chapter 4

Yau ma da bakin ciki ta tashi dan sam barcin bai ishe ta
ba,hakan nan ta shirya ta samu su Anti farida suna
karyawa,sama2 suka yi tadi driver ya wuce dasu school.
Amma data dawo da murnar ta dan yau sun gama exams
se kuma jiran result.
____
10:00 Zulfa'u ta yi wanka cikin wasu riga da skirt kalar
maroon,irin shigar nan tata data saba se ta daura black
vail ta sauko qasa.
A parlour ta tarrar da Anti farida dake fama dasu fudel
kasancewar weekend ne.
Zama tayi a kujera tana fadin
"Fudel zo"
Da gudu kowa yazo ya hau kan cinyar ta yana dariya tana
shafa kansa tace
"Abar mommy ta huta koh?"
Daga mata kai yayi yana wasa da button din rigar ta yana
fadin
"Mum let's go shopping today"
Hada ido da Anti farida suka yi nan da nan suka sa dariya
Zulfa'u tana jan hancin sa tace
"Ba yau ba,mu jira daddy ya dawo gobe se muje shopping
koh?"
Nan suka hau murna suna tsalle dan baban su bai fiye
zama a gida ba yawanci yana tafiye2 dan costume ne
Allah ya bashi arziki.
"Yawwa Zulfa'u tashi kije wajen maman habiba ki kai mata
wannan kice gashi na manta ban kawo mata ba tun jiya
se yau na samu"
Wani dan bowl ta miqo mata
"Anti farida wannan din menene?"
"Kanwa ce mana,ki tashi ki kai mata kina wasting time tun
jiya fa ta tambaye ni da safe"
Tashi tayi hade da daukar bowl din tayi site din.
Tana zuwa bakin qofar ta danna door bell wajen sau uku
tana dannawa daga ciki taji ana fadin
"Come in"
Shiru tayi na wasu seconds dan idan bata manta ba irin
muryar nan taji jiya amma se kawai ta murda handle din
hade da yin sallama.
Tsayawa tayi tana bin parlourn da kallo dan komai an
canja se dai iri daya ne da nasu se din canja canja da ba'a
rasa ba.
Kudi da suna magana da tuni nan gidan ya fara dan ya
tsaro iya tsarowa ba shirgi se komai da yake a mazaunin
sa.
A cikin seconds din da basu gaza 6 ba ta qarewa parlourn
kallo sannan ta maida kallon ta ga kujerar da mutumin
dake zaune wanda hannun sa riqe da Mug da alama
coffee yake sha.
Riga ce T-shirt a jikin sa se wando iya gwaiwa,ya hakimce
a kan kujerar idon sa kan tv.
Kasa dauke idon ta tayi a kansa dan fari ne wanda ya
matukar dacewa dashi.
Iya kyau ya hadu dan kyakkyawa ne nesa ba kusa ba
kuma shigar da yayi seya qara fiddo da ainihin surrar jikin
sa da take a murde kamar body builder,duk da bawai kato
bane amma baza a ce masa siriri ba kansa ya tara suma
da kuma saje daya zagaye kyakkyawar fuskar tasa wuyan
sa sanye da chain kana gani kuma kasan gold ce.
Bai amsa mata sallamar ba hasalima miqewa tsaye yayi
yana shan coffee dinsa hankali kwance kamar bai san da
ita a wajen ba.
Nan da nan ran Zulfa'u ya baci gannin yadda ya maida ita
tamkar wata gunki a wajen.
"Wa'alai kumussalam"
Salamar da aka ansa ne daga saman stair case din yasa
Zulfa'u maida kallon ta wajen.
Wata mata ce ta fito sanye da atampa blue wacca ta
matukar yi mata kyau dan fara ce sosai kana gannin ta
kasan sun hada jini da wanda ke zaune a kujerar.
Dan murmushi Zulfa'u tayi bayan matar ta iso inda take
wanda itama murmushin bai bar fuskar ta ba.
"Emmata"
Daga jin yadda ta fadi emmatan kasan hausar bata zauna
sosai a bakin ta ba,dan murmushi Zulfa'u tayi tana fadin
"Good morning ma"
"Morning how're u?"
"I'm fine"
Sannan ta miqa mata bowl din tana fadin
"Gashi tace na kawo miki tace kiyi hakuri mantawa tayi"
Karba tayi tana fadin
"Oh Allah sarki kice mata na gode"
Murmushi tayi sannan ta dan kalli shi yana nan tsaye a
wajen,se a sannan taga tsayi ne dashi bana wasa ba dan
dogu ne sosai masa Allah se ya qara masa kyau nesa ba
kusa ba.
"What's ur name?"
"Zulfa'u"
Dan murmushi tayi tana fadin
"You have a nice name and u look alike u resemble each
other,is she ur sister?"
Dan murmushi tayi tana daga mata kai alamun eh sannan
tace
"Thank u ma"
Dafa kafadar ta tayi sannan tace
"Jira bari na kawo miki bowl din"
Juyuwa tayi tana kallon saurayin dake tsaye yana kallon tv
tace
"Honey take this to the kitchen"
Juyuwa yayi yana kallon ta ba tare da ya kalli Zulfa'u dake
tsaye a gefen ta ba yace
"Ok mum i'm coming"
Dan bata fuska tayi tana fadin
"Baka iya yiwa baki magana ba,can't u say hi to our
neighbour,Zulfa'u"
Kallon sa ya kai kan Zulfa'u dake tsaye a wajen har a
lokacin tana binsa da kallo yace
"Hi"
Sannan tace
"Meet my son Christoph"
Kallon sa take sannan tace masa itama
"Hi"
Bata fuska tayi tana fadin
"Haka ake gaishe da baki a garin ku koh?"
Dafe kansa yayi yana fadin
"Oh Gosh Anti Mary,what did u wan me to say again?"
Kawai ya karbe bowl din yayi kitchen dashi Zulfa'u ta raka
shi da ido hade da tabe baki.
Murmushi tayi tana kallon Zulfa'u hade da rage murya
tana fadin
"Yaran zamani"
Itama dan murmushi tayi,yana fitowa daga kitchen din ya
miqa mata sannan yayi stair case din dan gudu2 har
ginnin yana dom dom yaji takon maza.
"Ya school?"
Ta fada tana kallon Zulfa'u
"Alhamdulillah muna hutu"
Kallon ta sosai take sannan tace
"Ohkay kuna hutu shiyasa bana gannin ki sosai amma zaki
na shigowa koh?"
Daga mata kai tayi tana fadin
"Eh zan na shigowa"
"Yawwa baby girl kice mata na gode sosai koh?"
Daga mata kai kawai tayi sannan tayi ficewar ta,amma
tana mamakin dan ta ne wannan gardin.
Shigowa parlourn tayi da sallama se data zauna sannan
tace
"Tace ta gode"
Murmushi Anti farida tayi tana fadin
"Kinga maman habiba yau tana da kirki koh?"
Dan murmushi tayi tana jinjina kanta alamar eh,amma
har yanzu tunanin su bai bar brain dinta ba.

Kaddara ta chapter 3

KADDARA TA Chapter 3

Tunda ta dawo tayi shigewar ta daki koda Anti farida ta
duba dakin gani tayi tana bacci,murmushi tayi sannan ta
isa bakin gadon tana taba qafar ta,da kyar ta miqe zaune
tana mitsitstika ido
"Bacci haka kamar wata kasa"
Mika take yi cike da shagwaba tana fadin
"Oh Anti farida "
Dariya take tana fadin
"Wake up wake up,tashi kiyi wanka kici abinci tun dazu fa
kike bacci ga can babies dinki sun dame ni ina mum take"
"Anti farida bar ni nayi bacci yau da ciwon kai na tashi tun
safe"
"A'ah bacci ya qare se na dare kuma"
Badan taso ba haka ta tashi ta shiga toilet tayi wanka
bayan ta fito ta saka dugowar riga ta dawo down stairs.
Suna gama cin abinci Fausam da Fudel suka zagayeta se
da ta musu assignment dinsu.
Da dare after isha'i tana daki ta kira maman su tana
picking suka gaisa se shagwaba take zuba mata
"Mama nidai gaskia wannan hutun kano zan dawo"
Girgiza kanta ta fara kamar a gaban Zulfa'u maman nata
tana fadin
"A'ah Zulfa'u kar ma ki fara,kiyi zaman ki anan
concentrate on ur studies,ki fito da result me kyau
wannan karon ma.kinji koh?"
Badan taso ba tace toh,suka yi sallama ta kira Salim,yana
dauka yace
"Hello babe"
Kwanciya sosai tayi akan gadon kana ta turo baki kamar
yana gaban ta tace
"Hi"
'yar dariya yayi yana fadin
"Yau 'yar shariya ce ba'a son yi min magana,bayan ni ne
yakamata nayi fushi kwana da kwanaki an manta ni"
Shiru tayi masa shi kuma ya cigaba da fadin
"Ok toh i'm sorry sweetheart bazan qara ba"
Murmushi ne ya subuce mata wanda se daya ji hakan
yasa shima dadi ya kama shi yana fadin
"Yawwa sweetheart dafantan dai an daina fushin dani?"
"Eh"
Girgiza kai yayi kaman yana gaban ta sannan suka shiga
tadi kamar basu ne suka gama fada yanzu ba.
Salim saurayin Zulfa'u ne wanda tun suna secondary yake
sonta har ma a gida an san da maganar su auren me dai
har yanzu ba'a yi ba suma anan Abuja suke da zama.
A cikin week din nan suka fara exams dan ta ajiye komai
a gefe karatu kawai take dan Zulfa'u badaga nan ba wajen
karatu.
Suna tsaka da exams Ummi ta kira ta tana zaune a daki
tana duba wasu books wayar ta tayi qara,dauka tayi tana
fadin
"Hello Ummi"
Shiru tayi tana jin ta daga baya tace
"Okay se kin shigo"
Tana nan zaune taji sallamar Ummi se dai bata kawo suna
tare da su Mary ba,da sauri ta sauko daga stairs din tana
ji suna gaisawa da Anti farida gabaki dayan mood dinta ya
canja hakan nan dai ta sakko ta same su itama ta zauna
kusa da Ummi suka fara gaisawa."Karatu fa yau nake so ki koya mana dan kinsan ba iyawa
nayi sosai ba"
Ta dan tsuke baki Zulfa'u tana fadin
"Me fa?"
Zaro ido Ummi tayi tana fadin
"Exam din da muke dashi gobe mana,pol science kema fa
kin san ban iya sosai ba"
"Su basu iya bane da baza su koya miki ba?"
Zulfa'u ta fada hankalinta kwance,sosai Ummi ke kallon ta
tana fadin
"Zulfa'u bana son rashin mutumci inkin san baza ki iya
koya mana ba se mu tashi muyi tafiyar mu"
Duk bidirin nan da suke yi a iya tsakanin su ne dan Anti
farida se tadi take dasu Mary.
Tabe baki tayi sannan ta tashi tace
"I'm coming"
Binta da kallo Ummi kawai tayi,ta dawo hannun ta da
books dinta sannan ta kalli Anti farida tana fadin
"Anti za muje compound muyi karatu"
Carpet me dan girma ta dauko musu hadda drinks da
snacks suka nufi compound din.
Kasancewar rana tayi sanyi se suka nemi gefen flowers
suka yi zaman su.
Gabadaya a takure Zulfa'u take sam bata son hulda da su
amma badan taso ba tana cin magani tana komai haka ta
koya musu.
Bayan sun danyi karatun na tsawan 1hr suka dan fara tadi
wanda Zulfa'u kam bata saka musu baki se dai tayi yake
ko kuma tace eh ko a'ah
"Gaskia ur Anti is nice,tana da kirki sosai i like her gata
me kyau,she's beautiful kamar babies dinta"
Inji Ada,dan murmushi tayi Zulfa'u kana ta maida hankalin
ta kan wayar ta da take dannawa.
Bude gate din da aka yi ne yasa su maida kallon su kan
katuwar motar data shigo land cruiser kalar dark brown
kamar sabuwa,sosai suke bin motar da kallo wanda
Zulfa'u kam hankalin ta yana kan wayar ta da take
dannawa dan ta bawa gate baya.
"Zulfa'u yaushe kuka yi new neighbours?a iya sani na
maman jafar sun tashi tunda jimawa"
Inji Ummi ta fada still idon ta yana kan motar
"Basu jima da zuwa ba"
Ta bata amsa,bude kofar motar aka yi wanda lokaci daya
zaka ji yadda suke dariya da tadi da alama bama hausawa
bane jin yadda suke dariya kamar zasu fasawa Zulfa'u
kunne.
Juyuwa tayi hade da kai kallon ta kan motar wanda tun
shigowar su se yanzu ta samu gannin su ta cikin glasses
dinta.
Lokaci daya taji zuciyar ta ta buga wanda hakan ya zama
bakwan lamari a tattare da ita dan wadan da ta gani ba
karamin bugun zuciya taji ba.
Kana gannin su kaga riqaqqun cristains,su 5 ne wanda
duk kallon da kayiwa daya daga cikin su kasan akwai ji da
samar taka da kuma kudi,kamar wasu masu aykin qarfi
dan a murde suke dan ko ba'a fada ma kasan suna
ziyartar gym.
Daga me chain a wuya se me dan kunne da sarqa wanda
duk cikin se ba mai shigar kirki daga me wando iya
gwaiwa se riga wancca tasa thick muscles dinsu bayyana.Har suka shige dayan flat din Zulfa'u bata daina binsu da
kallo ba,tambayar kanta take dama neighbours din nasu
Christians ne?
"Wow the look Aderobale"
Muryar Mary ce ta dawo da ita daga tunanin data
fada,lokaci daya kuma ranta ya qara baci dan jin abinda
Mary ta fada
"Amma neighbours din nan naku suna da kyau they look
handsome bayan hakan ma suna da kudi"
Ji tayi kamar ta kife Mary da mari lokaci daya ta hau
tattara books din tana fadin
"I think i will be going inside"
Suma tashi suka yi Ummi tana fadin
"Muma wucewa za muyi"
Se da suka gama maida kayan suka yiwa Anti farida
sallama sannan ta rako su bakin gate,Ada tace
"Thank u"
Dan murmushi tayi tana gyara zaman eye glasses din nata
suka wuce Ummi tana daga mata hannu tace
"Bye see u tomorrow"
"See ya! "
Se data ga wucewar su sannan ta koma ciki amma idon ta
yana kan motar da tayi parking.
A parlour ta samu Antu farida ta fada kan kujera tana
fadin
"Washh !"
Dariya Anti farida ke mata tana fadin
"Lazy kawai se kace wanda tayi wani aiki"
Murmushi kawai tayi tana shafa kan Fausam dan har
yanzu tunanin neighbours din nasu bai bar brain dinta ba.
Bayan sunyi dinner a parlour suna zaune kafin ta wuce
daki ta kalli Anti farida tana fadin
"Anti dama neighbours din mu ba musulmai bane?"
Dan girgiza kai tayi tana fadin
"Ba Christians bane musulmai ne dan sunan matar gidan
Maryam itama tama da en yara su biyu mace da namiji
kamar fudel da fausam"
Sosai Zulfa'u take binta da kallo tana mamakin kuma
wadan da suka zo dazu watakila baki ne
"Me kika gani?"
Da sauri ta girgiza kai cikin zuciyar ta tana fadin toh ma
ina ruwa na dasu?
"Kema fa yakamata kije ku gaisa da ita dan tana da kirki
sosai"
"Insha Alllah zanje"
"Yaushe ne gama exams din naku?se next week koh?"
Cike da tsoro Zulfa'u ta kalli Anti farida lokaci daya suka
sa dariya tana fadin
"Ki rufa mana asiri Anti ai se abun ya mana yawa,gobe
insha Allahu za mu gama"
Dariya tayi tana fadin Allah ya sa aga result me kyau,10:40
nayi ta wuce daki ta fara shirin bacci.
Tana tsaye a gaban mirror taji hayaniya a compound din
nasu,kasancewar ta window nata ana kallon tsakiyar
compound din yasa ta leka.
Wadan nan din dai ta hango sun zo bakin motar suna
magana wanda har Zulfa'u dake binsu da kallo tana dan
jiyu wasu abubuwan,kana jin yadda suke magana kasan ba
hausawa bane.
Su 4 ta gani sun shiga motar,shi kuma yana tsaye a wajen
har motar su ta fice.
Sosai Zulfa'u take son kallon fuskar sa amma bata ganshi
ba dan babu haske sosai a tsakiyar compound din,tana
gannin sa har ya koma ciki.
Tsaki taja kana ta kashe wuta hade da kwanciyar ta,5mins
yayi yawa bacci ya dauke ta.
Kamar daga sama ta fara jin kida wanda yasa ta tashi
zaune tana duba agogon dake side rower nan da nan ta
hau jan tsaki dan karfe 11:58 ya nuna mata
Eye glasses dinta dake ajiye kan side drower ta saka hade
da tashi ta leka window ta hango window ndake kallon
nata taga wutar a kunne amma gabadaya wutar site din
ma a kashe take.
Hakan nan yau ma tayi bacci rabi da rabi.